Ehlibeyt (as) Haber Ajansı ABNA - Majiyar ‘yan jaridar kasar ta Mali ta ce wani sashe na masu Zanga-zangar sun kunna wuta a wani sashe na ginin majalisar dokokin kasar tare da lalata shi, kuma mutum guda ya rasa ransa.
Har ila yau masu Zanga-zangar sun kutsa cikin ginin Radio da talabijin din kasar a birnin Bamako da hakan yayin sanadiyyar dakatar da watsa shirye-shirye.
Al’ummar kasar Mali suna yi Zanga-zanga ne a matsayin matsin lamba ga gwamnatin shugaba Boubakar Kaita da ta yi sauye-sauye a bangarori daban-daban na harkokin yau da kullum na raywuar al’ummar kasar.
342/